Header Ads

Sojojin Sudan sun kai hare-hare ta jiragen sama a Khartoum, duk da cewa an tsaigaita wuta

Sudannna ci da wuta

Sojojin Sudan sun kai hare-hare ta jiragen sama a babban birnin kasar Sudan, Khartoum, kan sansanonin jami'an tsaron da ba sojoji ba duk da cewa sun amince da a kara wa'adin tsagaita wuta.

Sojojin sun bayyana cewa jiragen yakin su sun kai hari kan dakarun kai dauki domin tallafawa ayyukan tsaro (RSF)a Khartoum a ranar Alhamis.

Sojojin a yammacin ranar Laraba sun bayyana cewa sun amince da a tattauna a Juba, babban birnin makwafciyar kasar ta Sudan ta Kudu, a kan kara tsawaita wa'adin tsagaita wutar da aka yi na kwanaki uku wanda ya kawo karshe a ranar Juma'a karkashin jagorancin IGAD, wata kungiya ta kasashen gabashin Afirka.

An dai sha yin yarjejeniyar tsagaita wuta tun bayan barkewar fadan a tsakiyar watan Afirilu a tsakanin sojoji wadanda Janar Abdel Fattah al-Burhan ke jagoranta da kuma RSF, wadanda mataimakinsa wanda ya zama abokin gaba Mohamed Hamdan Daglo ke jagoranta.

Sai dai duka yarjejeniyoyin ba a yi nasara a cikinsu ba.

A yanzu dai mummunan fadan ya fadada daga babban birnin kasar zuwa yankunan kasar musamman yammacin Darfur, wanda dama ke fama da fadace-fadace.

Mutane kimanin 512 ne suka rasu a yayin da 4,193 suka raunata kamar yadda kididdigar ma'aikatar lafiya ta bayyana. Sai dai kididdigar yawan wadanda suka rasa rayukansu din ana zaton sun fi haka.

No comments

Powered by Blogger.