Header Ads

Masu zanga-zanga a Isra'ila sun sha alwashin cigaba

Sashin wasu masu zanga-zanga a Tel Aviv

Wata shugabar masu zanga-zanga a Isra'ila ta sha alwashin cigaba da gudanar da zanga-zanga a yankunan da Isra'ila ta mamaye a yayin da Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya sanar da cewa za a dakatar da yin canje-canje ga sashen shari'ar kasar har sai wata mai zuwa. 

"In har wadannan canje-canje sun cigaba da kasancewa ba wai dakatar da su aka yi ba, za mu kasance kan tituna." Shikma Bessler, wata shugabar masu zanga-zanga ta bayyana bayan Netanyahu ya gabatar da jawabi ta talabijin a ranar Litinin.

Bessler ta bayyana cewa Netanyahu da shi da ire-irensa a fili ya ke suna so ne su cigaba da dokokinsu na mulkin mallaka a cikin majalisar Knesset mai zuwa wadda za ta fara aiki nan da wata daya. 

Ta bayyana cewa canje-canjen, wadanda za su rage karfin kotu a kan sashen majalisar dokoki da sashen zartarwa, tare da ba majalisar Knesset ikon yin watsi da umarnin kotu da kuri'u 61 a cikin 120, na da cutarwa ga "Tattalin arzuki da tsaron Isra'ila."

Netanyahu ya bayyana a ranar Litinin cewa zai dakatar da kudurin yin canje-canje ga sashen shari'ar na dan wani lokaci. Amma ya bayyana cewa yana nan kan kudurinsa na yin canje-canjen.

Wannan dai hatsaniya ta kulle mafi yawan biranen kasar kuma tana yin barazana ga tattalin arzuki, tsayar da tashar jiragen sama a babban filin jiragen sama na kasa-da-kasa na Ben Gurion sannan kuma ayyuka sun tsaya a tasoshin jiragen ruwa.

An kulle makarantun yara, shaguna da reshen shagunan sayar da abinci wanda aka sarrafa.

Wannan fafutika a kan shirin canje-canjen na yin nuni ne da irin darewar da ke tsakanin al'ummar Isra'ila tsakanin masu goyon bayan gwamnati, wadanda suka ce canje-canjen na da muhimmanci, da kuma mutanen da suka fi yawa wadanda basu goyon bayan shirin na Netanyahu, wadanda suka ce wannan al'amari zai rage karfin bangaren shari'a ne.

No comments

Powered by Blogger.