Gobarar Kasuwar Singer: Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima Zai Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kano
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci Mataimakin sa, Kashim Shettima, da ya jagoranci wata babbar tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Jihar Kano domin jajanta wa ‘yan kasuwar da gobarar Kasuwar Singer ta shafa. Ana sa ran tawagar za ta tashi daga Abuja yau domin isar da saƙon ta’aziyyar Shugaban Ƙasa ga ‘yan kasuwar da suka…
Shugaba Tinubu Ya Jajanta wa ‘Yan Kasuwar Kano Kan Gobarar Kasuwar Singer, Ya Ba da Umarnin Bincike
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya jajanta wa ‘yan kasuwa da al’ummar Jihar Kano sakamakon gobarar da ta tashi a Kasuwar Singer a ƙarshen makon nan. Gobarar, wadda ta fara da yammacin ranar Asabar, ta ci gaba da ƙonewa har zuwa safiyar Lahadi, inda ta haddasa mummunar asara musamman a sashen sayar da kayan abinci…
Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Yola, Tare da Kaddamar da Ayyuka
Shugaba Bola Tinubu zai kai ziyarar aiki ta yini guda zuwa Jihar Adamawa a ranar Litinin, kasa da awanni 48 bayan makamanciyar ziyarar da ya kai Jihar Kebbi. A yayin ziyarar, Shugaban kasar zai kaddamar da wasu muhimman ayyuka da aka kammala tare da ganawa da manyan jami’an gwamnati da kuma sarakunan gargajiya na jihar….
Jaridar NEW TELEGRAPH Ta Karrama Gwamna Lawal Da Lambar Yabo Ta Gwamna Mafi Nagarta Na Shekarar 2025
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu lambar yabo ta Gwamna Mafi Nagarta na Shekarar 2025 daga jaridar New Telegraph, saboda fitattun ayyukan sa na ci gaba a jihar. Gwamnan ya karɓi wannan lambar yabo ne a ranar Juma’a, yayin bikin raba lambobin yabo da liyafar dare da jaridar ta shirya a babban ɗakin taro…
Gwamnatin Tarayya ta ƙarfafa tsaro a Arewa-ta-Tsakiya bayan harin Kwara – Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙarfafa ayyukan tsaro a yankin Arewa-ta-Tsakiya bayan hare-haren da suka yi sanadin mutuwar kusan mutane 75 a Jihar Kwara. Idris ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a. A cewar sa, sabon farmakin tsaron,…
Gwamna Lawal Ya Lashe Kyautar Gwarzon Gwamnan Shekara Ta Jaridar LEADERSHIP, Ya Sake Jaddada Ƙudirin Ci Gaban Zamfara
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake tabbatar da ƙudirin gwamnatin sa na kawo sauyi mai ma’ana da farfaɗo da ƙwarin gwiwar al’umma ga harkokin mulki a jihar. Gwamnan ya karbi Kyautar “Gwarzon Gwamnan Shekara” ta jaridar LEADERSHIP a ranar Alhamis, yayin taron shekara-shekara na jaridar da aka gudanar a Cibiyar Taron Ƙasa da Ƙasa…
CBN ya umurci bankuna su riƙa sayar wa ‘yan canji dala 150,000 kowane sati
Ashafa Murnai Barkiya Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bai wa masu lasisin hadahadar canjin kuɗi (BDC) damar samun kuɗaɗen ƙasashen waje daga Kasuwar Canjin Kuɗaɗen Ƙasashen Waje ta Nijeriya (NFEM) ta hannun bankunan da aka ba izini. CBN ta sanar da hakan ne a ranar Talata cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun Musa…
SHUGABA TINUBU YA NAƊA AMB. ISMAIL ABBA YUSUF A MATSAYIN SHUGABAN NAHCON
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a matsayin sabon Shugaba kuma Babban Darakta (Chairman/CEO) na Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON). Naɗin na jiran amincewar Majalisar Dattawa kamar yadda Sashe na 3(2) na Dokar NAHCON ta shekarar 2026 ya tanada. A cikin wasiƙar da ya aikewa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio,…
Tinubu ya naɗa Magaji Da’u Aliyu a matsayin shugaban cibiyar binciken nukiliya ta ƙasa, ya kuma sabunta shugabancin NEMSA
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Hon. Magaji Da’u Aliyu a matsayin Darakta Janar (MD) na Sheda Science and Technology Complex (SHESTCO), Abuja, cibiyar da ke da alhakin bincike da bunƙasa fasaha tare da kula da cibiyar binciken nukiliya ta ƙasa. Haka kuma, shugaban ƙasar ya naɗa Injiniya Adesayo Olusegun Michael a…
Asusun Ajiyar Kuɗaɗen Waje Na Nijeriya Ya Cika Maƙil Da Dala Biliyan 49 -Gwamnan CBN.
Ashafa Murnai Barkiya Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Olayemi Cardoso, ya tabbatar da cewa adadin kuɗaɗen waje da ke asusun ajiyar kuɗaɗen waje na Nijeriya, ya ƙaru zuwa dala biliyan 49, abin da ke nuna gagarumin farfaɗowa mai ɗorewa daga kusan dala biliyan 3 gwamnatin nan ta gada a watan Mayun 2023. Cardoso, ya bayyana cewa…
